SHUGABAN MAJALISAR DINKIN DUNIYA YA NADA AMAECHI BABBAN MUKAMI
Majalisar dinkin Duniya ta sanar da wani
muhimmin nadi da ta yi ma tsohon gwamnan jihar Ribas, kuma ministan sufurin
Najeriya, Chibuike Rotimi Amaechi, wanda ta nada shi mamba a kwamitin gudanarwa
na gidauniyar kiyaye haddura akan tituna na Duniya.
Jaridar Africanjournalist.info ce ta bayyana
haka a shafinta, inda tace majalisar ta sanar da nadin Amaechi ne a Geneva,
kasar Switzerland, wanda a yanzu haka ministan yana can kasar, inda yake
wakiltar Najeriya a taron gidauniyar dake gudana.
Majalisar ta nada Amaechi ne domin ya kirkiro
hanyoyin rage aukuwar haddura, rage adadin mutanen da hatsari ke rutsawa dasu
tare da tabbatar da tsaron lafiya da dukiyoyin mutane akan hayoyin Duniya gaba
daya.
Wata majiya a Najeriya ta ruwaito haidimin
Ministan akan kafafen watsa laabru, Israel Ibeleme yace tattaunarwa da ake
gudanarwa a yanzu haka a Geneva, da kuma shawarwarin da za’a yanke a can, zasu
taimaka matuka wajen ganin gidauniyar ta amfani al’ummar Duniya.
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku