SANATOCI 49 SUN NUNA ADAWA DA YUNKURIN TSIGE SARAKI DA EKWEREMADU
Akalla sanatoci 49 na tarayyar Najeriya
ne suka nuna adawarsu da yunkurin tsige shugaban majalisar dattawa Bukola
Saraki da mataimakinsa Farfesa Ike Ekweremadu.
Ku tuna cewa tun
a asubahin yau ne jami’an DSS suka mamaye majalisar dokokin Najeriya sannan
suka hana mutane shiga harabar majalisar. Haka zalika jami’an tsaron sun hana
yan majalisa da dama, musamman masu biyayya ga Saraki da Ekweremadu shiga
majalisar yayinda suka bar yan APC suka shiga.
Sanatan dake
wakiltan Bayelsa ta gabas Ben Murray-Bruce yayinda ya jagoranci sauran yan
majalisa wajen adawa da mamayar, yace sanatocin APC ne suka shirya hakan sannan
kuma cewa suna shirin tsige Saraki da Ekweremadu sannan su daura sanata
Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa.
Yace wannan
makirci da sanatocin APC ke shiryawa ba zai yi nasara ba domin jam’iyyar PDP ce
ke da masu rinjaye a majalisar dattawa.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku