MATAIMAKIN SHUGABAN APC NA OSUN YA JAGORANCI MUTANE 6,208 ZUWA ADP

Mataimakin shugaban jam’iyyar All Progressives
Congress a jihar Osun, Azeez Adesiji, ya jagoranci mambobin kwamitin jam’iyyar
na jihar su takwas da mambobin jam’iyyar 6,200 na kananan hukumomi da mazabu
zuwa jam’iyyar Action Democratic Party.
Shugabannin APC da mabiyansu sun samu tarba
daga shugaban jam’iyyar APD, Toye Akinola a sakatariya jam’iyyar dake Osogbo
cikin farin ciki. Adesiji yayi zargin cewa dalilin su na sauya sheka ya kasace
saboda son kai da halin rashi kula na masu yanke hukunci a APC da kuma yadda
gwamnatin jhar ke yi da jama’a ajihar. Shugaban jam’iyyar ADP a jihar, Toye
Akinola yace ya ji dadin sauya shekar yan siyasa daga jam’iya mai mulki zuwa
jam’iyyar adawar.
Yace wasu yan jam’iyyar APC sun sanar da shi
cewa suna nan dawowa jam’iyyar kwanan nan. Ya bukaci mutanen jihar da su marawa
dan takarar gwamna a jam’iyyar Moshood Adeoti vaya domin cewa shine zai ceto su
daga wahalhalun da suke ciki.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku