DRAMANI MAHAMA ZAI SAKE TSAYAWA TAKARAR SHUGABANCIN GHANA
Tsohon shugaban Ghana John
Dramani Mahama, ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a zaben shugabancin
kasar da za’a yi a cikin shekaru biyu masu zuwa.
Mahama, wanda ya mulki
kasar tsawon shekaru 4 daga 2012 zuwa 2016, ya gaza samun nasara a zaben
shugabancin kasar da ya gudana a shekarar ta 2016, wanda abokin hamayyarsa wato
shugaba mai ci Nana Akufo-Addo ya lashe.
Tsohon shugaban na Ghana ya
bayyana aniyar tasa ce a sakon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya ce
tuni ya mika takardar neman izinin jam’iyyar adawa ta NDC ta tsayar da shi
takara.
A tsakanin watan Oktoba
zuwa Nuwamba jam’iyyar NDC za ta gudanar da zaben fidda gwani tsakanin masu
neman ta basu takarar shugabancin Ghana tsakanin tsohon shugaban kasar, John
Dramani Mahama, da kuma sauran masu neman takarar guda 4.
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku