BUHARI YA YI FATAN ALKHAIRI GA MASU SAUYA SHEKAR SIYASA A NAJERIYA




Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya aike da sakon fatan alkhairi ga Ilahirin ‘yan siyasar da suka sauya sheka daga wata jam’iyyar zuwa wata a dai dai lokacin da babban zaben kasar ke karatowa.



Muhammadu Buhari yayin wani taron cin abinci rana da ya gudana tsakaninsa da gwamnonin Jam’iyyar ta APC ya ce kowanne dan siyasa na da dalilin sauya sheka zuwa wata Jam’iyya.
A cewar shugaban na Najeriya, sauya shekar ta wasu jiga-jigan siyasa a kasar ba zai kawo tsaiko ga ayyukan da gwamnatinsa ke yi don gina kasar ba.
A baya-bayan nan ne dai wasu tarin jiga-jigan Jam’iyyar ta APC suka sauya sheka zuwa babbar Jam’iyyar adawa ta PDP ciki kuwa har da shugaban Majalisar Dattijan kasar Bukola Saraki.
Sauran wadanda suka sauya shekar sun hada da Samuel Ortom Gwamnan Benue da Abdulfatah Ahmed Gwamnan Kwara da Godswill Akpabio tsohon Gwamnan Akwa Ibom.
Galibin dai masu sauya shekar sun nuna rashin amincewa da salon mulkin Muhammadu Buhari wanda ya karbi shugabancin a shekarar 2015.

 

 DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA 
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/  
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv  
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/

ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A  nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html

Comments