AKPABIO YA SAUKA DAGA SHUGABAN MARASA RINJAYE NA MAJALISAR DATTAWA
Shugaban
Marasa Rinjaye na Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya sauka daga mukamin sa.
Hakan ya biyo bayan komawar sa jam’iyyar APC daga PDP.
A
cikin wata wasika da ya aika wa Sanata Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye,
Emmanuel Bwacha, Akpabio ya ce ya sauka tun daga ranar 4 Ga Agusta, 2018.
Ya gode wa shugabannin majalisar
ta dattawa da har suka ba shi damar shugabancin marasa rinjaye na tsawon
shekaru uku da ya yi.
Akpabio, wanda shi ne tsohon
gwamnan jihar Akwa Ibom, ya garzaya Landan inda Shugaba Muhammadu Buhari ke
zaman hutu ya je ya yi mubayi’ar komawa jam’iyyar APC daga PDP.
Bayan dawowar sa Najeriya kuma,
Akpabio ya ziyarci jagoran APC, Bola Ahmed Tinubu.
Ana sa ran yin gangamin karbar sa
a Ikot Ekpene, da ke Akwa Igbom.
Ya shiga APC dauke da shirgin
nauyin zargin harkallar danne wasu biliyoyin kudade.
Hawan Buhari mulki ke da wuya a
cikin 2015, Akpabio na daya daga cikin wadanda yaki da cin hanci da wawurar
kudade ya fara yi wa dirar mikiya.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku