EKITI: PDP ZA TA YI ZANGA-ZANGAN LUMANA NA GAMA GARI
Shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party
(PDP) ya umurci jami’an jam’iyyar na jihohi, shugabanni da masu ruwa da tsaki
da su yi zanga-zangan lumana a hukumomin yan sanda dake dukkanin jihohin
tarayya.
A wata sanarwa daga sakataren shirye-shirye na
jam’iyyar, Kanal Austin Akobundu (mai ritaya) a jiya, jam’iyyar ta bukaci
dukannin reshen tan a jihohi da su gabatar da wasikar zanga-zanga ga sufeto
janar na yan sanda, Ibrahim Idris ta hanyar kwamishinonin yan sandansu.
A kwanakin baya wadansu kafan yada labarai
sunruwaito cewa Kayode Fayemi, dan takarar gwamna karkashin jam’iyyar APC a
zaben Ekiti da za’a yi a ranar, Asabar ya ce yana so ya sake mulkar jihar ne
domin rage talauci a tsakanin mutane. Ya bayyana hakan ne a gangamin karshe da
APC ta yi gabannin zaben a filin wasa na Oluyemi Kayode dake Ado Ekiti a ranar
Talata, 10 ga watan Yuli. Mista Fayemi wadda ya yi gwamnan jihar daga 2010 zuwa
2014, ya bayyanawa taron jama’a cewa magajinsa, Gwamna Ayodele Fayose, ya
muzgunawa jama’ar jihar ta hanyar kin biyan albashi da fansho
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku