DAN KUNAR BAKIN WAKE YA KAI MUMUNAN HARI MASALLACI DA ASUBAN NAN
Wani dan kunar bakin waken yan kungiyar tada
kayar bayan Boko Haram ya kai mumunan harin kunar bakin wani masallaci da ke
Konduga a jihar Borno lokacin Sallar Asuba misalin karfe 5:15 na safe.
Wata majiya ta bayyanawa jaridar The Cable cewa
an hallaka masallata da dama kuma wasu sun jikkata. Yayinda jami’an tsaro suka
hallaro wajen a yanzu, an garzaya da wadanda suka jikkata asibiti. A yanzu dai
mutane takwas ne suka rasa rayukansu game da cewar wani dan CTJF a garin,
Ibrahim Liman, wanda yayi bayani ga manema labarai. Ya bayyana cewa dan kunar
bakin wake ne ya shigo masallacin misalin karfe 5:15 yayinda mutane ke Sallah
ya tayar da Bam.
Yace: “Wani dan kunar bakin wake ne ya shiga
masallacin misalin karfe 5:15 yayinda ake Sallah ya tayar da Bam. Ya kashe
mutane takwas tare jikkata wasu biyar.” Mutane bakwai suka mutu a take cikin
masallacin yayinda daya ya cika a hanyar asibitin Maiduguri.” Wani mazaunin
garin Umar Goni ya bayyana cewa yana hanyar zuwa masallacin ne Bam din ya tashi
kuma ya taimaka wajen ceton mutane tare da jami'an CJTF.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku