BELIN DASUKI: KOTU TA AIKA WA SSS DA MINISTAN SHARI’A SAMMACIN SU SAKI DASUKI
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta aika da sammacin a gaggauata sakin Sambo Dasuki. Ta aika sammacin ne ga Babban daraktan SSS da ake kira DSS da kuma Antoni Janar na Najeriya, Abubakar Malami.
A ranar Talata ne dai Dasuki ya cika sharuddan belin sa da kotun
ta bayar tun a ranar 2 Ga Yuli.
Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa ran talata ne da misalin karfe daya
na rana, mutane biyu da suka tsaya belin Dasuki tare da jami’in bada beli na
kotu, suka dunguma suka kai wa SSS da kuma Ministan Shari’a sammacin sanarwar a
saki Dasuki.
Duk da cewa masu karbar belin sun yi tsammanin cewa za a damka
musu Dasuki, majiya ta ce sai Darakatan SSS ya nemi iznin sakin sa daga fadar
shugaban kasa tukunna.
Sau takwas kotu na bada belin Dasuki, kuma sauk bakwai kotu na
kin bada belin sa.
Tun ranar talata ‘yan uwa da abokan arzikin Dasuki suka cika gidan sa su
na jiran isowar sa.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku