SHUGABANNIN JAM'IYYAR APC 11 DA AKA ZABA BABU HAMAYYA TARE DA OSHIOMHOLE

Jam'iyyar APC ta tabbatar da tsohon shugaban kungiyar kwadago na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Edo, Kwamared Adams Oshiomole a matsayin sabon zababen shugaban ta na kasa






Mr Oshiomole ya yi nasarar zama sabon shugaban jam'iyyar ne cikin sauki saboda dukkan sauran abokan takararsa sun janye. Kazalika haka ragowar shugabannin jam'iyyar 11 aka zabe su ba tare da abokan hamayya ba, ta hanyar yin sulhu tsakanin masu takarar kujeru daban-daban. Ga jerin sunayen su da mukaman su;

1. Ibrahim Masari,       -           Sakataren walwala.
2. Tunde Bello,            -           Sakataren kudi.
3. Zakari Mohammed  -           Sakataren jam'iyya na yankin arewa ta tsakiya.
4. Hassana Abdullahi, -           Shugabar mata ta yankin arewa ta tsakiya.
5. Nelson Abba,          -           Ex-officio na yankin arewa ta tsakiya.
6. Abubabakr Ajiya,    -           Sakataren jam'iyya na yankin arewa maso gabas.
7. Isa Azare,               -           Ex-officio na yankin arewa maso gabas.
8. Tukur Gusau,          -           Sakataren jam'iyya na yankin arewa maso yamma
9. Nasiru Haladu,        -           Ex-officio na yankin arewa maso yamma
10. Mrs Rachael         -           Akpabio, Shugabar mata ta yankin arewa ta kudu maso kudu
11. Misbahu L Didi,     -           Wakilin masu bukata ta musamman

Da akwai yiwuwar ta hanyar sulhu za a fitar da ragowar shugabannin jam'iyyar 42 kamar yadda aka sanar da wadannan ya zuwa yanzu.




Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta


Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com

Comments