BUHARI YA AMINCE DA FITAR DA BILIYAN N10BN DOMIN TALLAFAWA MUTANEN FILATO DA RIKICI YA SHAFA



Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana iftila’in gobarar tankar dakon man fetur da ya faru a Legas a mastayin daya daga cikin manyan annoba da suka faru a Najeriya a baya-bayan nan.
Shugaban kasar ya bayyana haka ne cikin wani jawabi da kakakinsa, Malam Garba Shehu, ya raba ga manema labarai a Abuja. Buhari ya bayyana cewar lamarin ya matukar girgiza shi da nuna alhininsa bisa asarar rayuka da dukiya da gobarar ta haifar.
Da yammacin yau Alhamis ne wata babbar motar tanka ta kama da wuta a gadar Otedola dake wajen jihar Lagas, a kan babbar hanyar zuwa Ibadan.
Rahotanni sun bayyana cewa hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASEMA) da hukumar kashe gobara ta jihar sun gaggauta zuwa wurin da abin ya afku. Kazalika rundunar ‘yan sanda ta ko-ta-kwana (RRS) ta ce ta tura jami’anta domin shawo kan lamarin. Saidai karfin wutar ya yiwa gaske saboda kasancewar motar na dauke ne da man fetur, sannan motocin dake kusa da wurin suma duk sun kama da wuta. A cewar shaidu da abun ya afku a idanunsu, sunce wutar ta lashe sama da motoci 20 da kuma wasu mutane da ba’a san adadinsu ba akan gadar ta Otedola dake kan babban titin Legas zuwa Ibadan.




Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta



Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com 

Comments