RUNDUNAR SOJI SUN KAWAR DA YAN BOKO HARAM 3 SUN KWATO MAKAMAI
Yan
ta'addan Boko Haram sun sha gagarumin kaye yayinda sojojin Najeriya suka kai
masu harin bazata harma an kashe uku daga cikin yan ta'addan.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa tayi
nasarar kawar da yan ta’addan Boko Haram uku a wani harin bazata a kauyen Mayanti
dake karamar hukumar Bama na jihar Borno a ranar Juma’a, 24 ga watan Agusta.
Birgediya Janar Texas Chukwu, daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin ne ya
bayyana hakan a wata sanarwa da ya saki a Maiduguri a ranar Juma’a. Ya bayyana
cewa rundunar bataliya 151 ne suka hallaka yan ta’addan.
Chukwu ya bayyana cewa an kwato makamai daga
hannunsu wadanda suka hada da bindigar AK47, Mujalla uku, alburusai 32, babur
daya da wayoyin android biyu.
Ya bayyana cewa ana kokarin kama sauran
mambobin kungiyar yan ta’addan.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku