MATAIMAKIN GWAMNAN JIHAR KANO HAFIZ ABUBAKAR YA AJIYE AIKIN MATAIMAKIN GWAMNA
A jiya Lahadi ne mataimakin
gwamnan jihar Kano Hafiz Bello ya mika takardar ajiye aiki wato sauka daga
kujerar mataimakin gwamnan jihar
Kakakin Hafiz, Abdulwahab Ahmad ne
ya mika wa PREMIUM TIMES kwafin takardar.
A
cikin takardar, Hafiz ya bayyana cewa sam baya jin dadin yadda suke aiki da
gwamnan jihar Abdullahi Ganduje.
”
Kwata-kwata gwamna Ganduje ba ya daraja kujera ta na mataimakin sa. Ko na bada
shawara ba ya dauka da hakan yasa muka fada cikin kamayamayar da jam’iyyar ta
shiga a yanzu a jihar.
”
Na yi ta fama da bakin ciki, zaman maraici da kakanikayi duk a dalilin rashin
daraja ni da kujerar da nike zaune a kai. A haka ne na yi shawara sannnan na
yanke hukuncin hakura da aikin kawai.
Shi
dai Hafiz Abubakar makusancin sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da ake ganin nan ba
da dadewa ba zai canza sheka ya koma PDP.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku