KASASHEN DUNIYA NA CI GABA DA JIMAMIN MUTUWAR KOFI ANNAN
Kasashen duniya na cigaba da nuna alhini dangane da rasuwar tsohon babban magatakarda na MDD Kofi Annan, wanda ya rasu a yau asabar yana da shekaru 80 a duniya.
Mista Annan ya jagoranci
Majalisar dinkin duniya tsakanin 1997 zuwa 2006, kuma shi ne dan asalin Afirka
bakar fata na farko da ya taba rike wannan mukami a cikin wani yanayi da duniya
ke fama da ringingimu iri iri.
Ana dai bayyana Mista Annan
dan asalin kasar Ghana a matsayin daya daga cikin wadanda suka gudanar da
jagoranci nagari a majalisar.
Gwamnatin Ghana ta sanar da
ware tsawon mako daya domin zaman makoki samakon wannan rashi, yayin da
kasashen duniya suka bayyana Kofi Annan a matsayin jagora abin koyi.
Shugaban Faransa Emmanual
Macron ya bayyana shi da cewa mutum ne da ya yi gwagwarmaya a duk tsawon
rayuwarsa, kamar dai yadda shugaban Rasha Vladimir Putin ke cewa dattijo ne
kuma mai kuzari.
Jakadiyar Amurka a MDD
Nikki Haley, ta ce har kullum duniya za ta cigaba da tuna tsohon babban
magatakardar na Majalisar, yayin da Antonio Gueterres ya bayyana marigayin a
matsayin da cewa mutum ne da ya yi jagoranci zuwa ga tarfaki nagari.
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku