HANKULAN SHUGABANNIN SIYASA BAI KWANTA DA GWAMNATIN BUHARI BA - OKOROCHA


Gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha ya bayyana cewa hankulan shugabannin siyasa a kasar bai kwanta da gwamnatin shugaban kasa Muhammad Buhari ba don haka suka hade masa kai.



Gwamnan wadda ya kara da cewa shugaban kasar bai aikata aibu a garesu ba, ya bayyana cewa shugabanni na tsoron a hukunta su akan rashawar da suke yi hakan ne yasa suka hadewa shugaban kasar kai.
Gwamnan yace shugaban kasar ya yarda da al’umma sannan kuma ya yarda cewa dole a yi taka tsantsan da arzikin kasar don jama’a su amfana daga gare shi, inda ya kara da cewa wadannan dalilai ne yasa shugabannin suke ganin bakin Buari sannan suna aikata hakan ne domin son zuciyarsu.
Gwamnan ya kara da cewa ya zama dole yan Najeriya su marawa shugaba Buhari baya domin yayi korari sosai wajen tsayawa kan gaskiya kuma bai amince da yin almubazaranci da dukiyar jama’a ba.


DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA 
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/  
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv  
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/

ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A  nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html

Comments