GWAMNATIN KANO ZA TA DAUKI MALAMAI MATA 1,196 A JIHAR
Gwamnatin
jiha Kano ta bada umurnin daukan malamai mata 1,196 da ke da kwalin kwalegin
ilimi a fadin jihar.
Kwamishanan matasa, raya al’adu da yada labarai
na jihar, Muhammad Garba, ya bayyana hakan ne a hira da manema labarai a jihar.
Gwamnatin jihar ta Kano ta umurci ma’aikatar
ilimin kananan hukumomi wato Local Government Education Authority (LGEA) ta
shirya takardun daukan aikin wadanda aka dauka da kuma sanya sunayensu cikin
asusun albashin gwamnati.
A bangare guda, makarantan horas da malamai
wato National Teachers Institute NTI ta bada umurnin amfani da kudi N450m wajen
horas da malaman ilimin lissafi da kimiya 500.
A cewarsa, wannan wani mataki ne
da gwamnatin jihar ke dauka wajen inganta ilimi da kuma tabbatar da cewa jihar
Kano na an gaba. Kana zai karfafa mata ta hanyar samar musu aikin yi a
ma’aikatar ilimin jihar.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku