BABBAR SALLAH: GWAMNATIN TARAYYA TA BAYYANA RANAKUN HUTU
Gwamnatin
tarayya ta bayyana ranakun Talata, 21 ga watan Agusta, da Laraba, 22 ga watan
Agusta a matsayin ranakun hutu domin murnar babbar salla (Eid-el-Kabir).
Ministan harkokin ciki gida, Abdulrahman
Dambazau, ne ya sanar da hakan yau, Alhamis, a Abuja a wata sanarwa da Umar
Mohammed, babban sakataren ma’aikatar ya sakawa hannu.
Gwamnatin tarayya ta taya ‘yan Najeriya murnar
zagayowar babbar sallar tare da yi masu fatan yin bukukwan sallah lafiya.
Kazalika, gwamnatin ta bukaci ‘yan Najeriya su rungumi soyayya da kaunar juna
domin samun zamana lafiya mai dorewa, kamar yadda Dambazau ya sanar.
Dambazau ya bukaci ‘yan Najeriya dake gida da
kasashen ketare das u cigaba da bawa gwamnatin shugaba Buhari hadin kai
musamman a kokarinta na tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a tsakani jama’a.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku