2019: AN CEWA DANKWAMBO YA HAKURA YA BARWA TAMBUWAL TAKARA
Alamu sun nuna a jiya cewa an sanyawa gwamnan
jihar Gombe kuma dan takarar kujerar shugaban kasa karkashin lemar Peoples
Democratic Party (PDP), Ibrahim Hassan Dankwambo, zafi cewa ya hakura da
kudirinsa gabannin zaben fid da gwani na jam’iyyar.
Jaridar NAIJ.com ta tattaro cewa Dankwambo
waanda ya bayyana kudirinsa na son takarar shugaban kasa makonni biyu da suka
shige na fuskantar matsin lamba daga wasu shugabannin siyasa da sarakuna a
yankin arewacin kasar kan ya hakura ya barwa gwamnan jihar Sokoto, Aminu
Tambuwal. Ku tuna cewa Tambuwal, wanda ya kasance tsohon kakakin majalisar
wakilai na daya daga cikin manyan yan siyasan da suka sauya sheka daga
jam’iyyar APC mai mulki zuwa PDP a kwanan nan.
Bincike sun nuna cewa dalilin zabar Tambuwal ya
kasance saboda yakinin cewa yana da dunbin magoya baya a fafutukar fiye da
Dankwambo. Majiyoyi na kusa da gwamnan sun fadawa majiyarmu ta Leadership cewa
sakamakon matsin lamba da yake samu da kuma goyon bayan da aka ba Tambuwal a
yanzu, Talban Gomben na duba ga neman takarar kujerar sanata na Gombe ta arewa.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku