WANI DAN SHEKARU 20 YA KASHE KANSA ‘A INDIA
Wani matashi mai shekaru ashirin (20) ya rataye kansa ‘a India.
Rahotanni sun bayyana ta wata majiya a yanar gizo cewa Lamarin
ya faru ne bayan da kasar Faransa ta doke Argentina daga wasan kwallon kafa na
gasar cin kofin duniya 2018 a Rasha.
Matashin wanda aka shaida shi da suna Halder ya kashe kansa ne a garin Habibpurda
ke yammacin Bengal’s Malda a India, ganin cewa shi masoyin dan wasan
kwallon kafan nan da yayi suna a wasan kwallon kafa (Messi). Bai zaci cewa
Argentina zata iya komawa gida ba, tsantsan bacin rai da tashin hankali, bai yi
jinkiri ba, sai ya shiga dakin say a kulle kofarsa da safiyar ran Lahadi inda
aka yi yunkurin bude kofarsa amma kash, bayan da ‘yan sanda suka balle kofar
tasa sai suka iske shi ya riga ya bakonci kiyama, gangan jikin sa tana lilo a
sama da igiyar da ta shake shi har sai da ya daina numfasawa.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku