TSARO: ATIKU NA GOYON BAYAN MAJALISA KAN BATUN 'YANSANDAN JIHOHI




- Wasu na ganin idan jihohi na da 'yansandansu za'a sami tsaro
- Wasu kuma na ganin gwamnoni zasu yi karfi sosai
- Atiku na bayan majalisa kan batun a baiwa jihohi dama a doka
Matsalar tsaro ta addabi jihohin kasar nan, inda ko wanne yanki yake fama da nasa, daga rikicin manoma-makiyaya, sai na kabilanci, sai na addinanci, da ma na siyasa, sai kuma na 'yan daba, da ma na 'yan fashi da masu garkuwa da mutane. A kuma bangare daya, akwai matsalar ta'addanci, inda Boko Haram ke kan ganiyar durkusar da kasar baki daya. Kokarin dawo da zaman lafiya ya sanya wasu ke ganin tunda gwamnatin Najeriya ta kasa, a baiwa jihohi damar su tsare jama'arsu da kansu.
Bayan da shuwagabannin majalisa suka nuna suna goyon bayan hakan, yanzu shima tsohon mataimakin shugaba Obasanjo, Atiku Abubakar, yace, ya dawo daga rakiyar gwamnatin tarayya, domin ta gaza tsare jama'a, don haka, a baiwa gwamnoni damar daukan jami'an tsaron jama'arsu a hukumance.


Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta


Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com

Comments