YAN BINDIGA SUN FAR MA KAUYEN MALIKAWA A JIHAR ZAMFARA
Rahoton da muke smau yanzun nan na
nuna cewa yan bindiga sun kai farmaki kauyen Malikawa a Gidan Gog, karamar
hukumar Maradun a jihar Zamfara.
A lokacin da muka samu wannan
rahoto, yan bindigan suna kan kashe mutane yayinda suka shiga kauyen suna
harbin kan mai uwa da wabi. Kungiyar Amnesty International ta bayyana hakan a
shafin sada zumuntar cewa: "Ana kan kai hari yanzu a Malikawa da ke Gidan
Goga, karamar hukumar Maradun na jihar Zamfara. Yan bindiga sun shiga kauyen
suna harbi." A watan Mayu, yan bindigan sun hallaka akalla mutane 30 a
kauyen Malikawan da wannan abu ke faruwa yau. Tun lokacin, mutan kauyen sun
kasance cikin fargaba. Za mu kawo muku cikakken rahoton..
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku