MATSALAR TSARO: 'YAN SANDA SUNYI SA'AR KAMA MASU ADDABAR JAMA'A HAR 37 A SASSAN AREWACIN KASAR NAN
Hukumar Yan sandan Najeriya ta sanar da cewa
jami'an tsa sunyi nasarar kama wasu gaggan 'yan fashi ga garkuwa da mutane guda
37 da suka addabi yankunan Arewacin Najeriya.
'Yan fashin wadanda suka kware wajen satar
mutane da kuma satar motoci, sun dade suna addabar matafiya a yankunan jihohin
Kaduna, Niger da Zamfara. Kakakin hukumar Yan sanda Jimoh Moshood ne ya gabatar
dasu ga manema labarai a ofishin yan sanda da ke Suleja.
Moshood ya ce hukumar ba za tayi kasa a gwiwa
ba wajen cigaba da sauke nauyinta na kare lafiya da dukiyoyin al'ummar
Najeriya.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku