KOTU TA BADA BELIN SAMBO DASUKI
Kotun
Koli ta Tarayya da ke zaune a Abuja ta ba da belin tsohon mai bada shawara kan
tsaron kasa, Colonel Sambo Dasuki (Mai Ritaya ).
Wannan
shi ne beli na shida da aka ba wa tsohon NSA. Duk da haka, ya kasance a
tsare a gidan tsare masu laifi na (DSS).
Mai
shari'a Ojukwu a ranar Litinin ta bayyana cewa, tsare Dasuki na tsawon shekaru
biyu da rabi na iya kawo cikas ga dokar kasa da kuma lafiyar sa.
Saboda
haka, ta bada belin Dasuki a kan Naira Miliyan Dari Biyu da Shaidu masu rattaba
hannu domin belin sa guda biyu.
Masu
belin sa dole ne su kasance Ma’aikatan gwamnati masu matsayi taku sha shida
kuma wadanda suka mallaki Filaye ko gidaje a Asokoro, Maitama, Utako ko Garki a
Abuja.
Har
ila yau, ana sa ran kowane mai yin belin Dasuki, sai biya Miliyan dari wa kotu
a matsayin kudin beli.
Saboda
haka, ta umarci DSS cewa, idan hukumar na so ta yi hira da Dasuki a nan gaba,
dole ne a yi ba tare da tsare shi ba, sa’an nan ya kasance ranar da ake aiki.
A nasa
bangare, tsohon Mai bada shawara ga Shugaban kasa a kan harkokin tsaro, Dasuki
ya roki kotu ta umarci DSS ta sake shi bayan shekaru biyu da rabi a tsare ba
tare da fitina ba.
Ya
kuma nemi kotun ta umarci DSS ta ba shi Naira biliyan biyar a matsayin babban
hasara, da kuma Babban Mai Shari'a na Tarayya ya nemi gafara a wurinsa domin domin
tsare shi da aka yi ba bias ka’ida ba.
Mai
shari'ar ta ce, duk da cewa an bada belin Dasuki, Kotu baza ta iya bada daman
bbiyan wani kudi ga dasuki a matsayin hasara ba.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku