KASAR CHINA ZATA YI WA NAJERIYA AGAJI DA RIGAKAFIN ZAZZABIN CIZON SAURO
- In dai maganin gargajiya ake magana, kasar Sin ta sanshi
- Magungunan zamani ma ba'a barta a baya ba
- Babu inda zazzabin sauro ke lahani a duniya irin Najeriya
Domin kawo karshen cutar nan mai hatsari ta
zazzabin cizon sauro a Najeriya, masana a bangaren lafiya daga jami'ar Jiangxi
ta magungunan gargajiya ta kasar China ta kawo sabon maganin cutar a Najeriya.
A wani taro da akayi a Legas, wanda ya samu halartar shuwagabannin cibiyoyin
gwamnati, masana daga China sunce sabon salon yaki da cutar ba wai da cutar
zazzabin cizon sauro zai yi yaki ba, har da ma wasu cutukan da suka zamo
barazana a Najeriya.
A lokacin da ake kwatanta maganin gargajiya na
Chanis din a matsayin magani mafi inganci gurin yaki da kalubalen da ake
fuskanta na lafiya, mataimakin shugaban masu duba marasa lafiya na China a
Legas, Duan Zhongqi, yace zasu cigaba da hada kai da hukumomin Najeriya don
cigaba da kawo ingantattun magunguna.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku