JERIN SUNAYEN ‘YAN MAJALISAR WAKILAI 37 DA SUKA FITA DAGA APC
Wani rahoto da muka samu da dumi dumi yanzun
nan ya tabbatar da cewa akalla mambobin majalisar wakilan Najeriya 37 ne suka
yi fatali da jam’iyyar APC mai mulki, suka kuma rungumi jam’iyyar PDP, ta
adawa.
Daga cikin ‘yan majalisar 37 da suka fice, 33
ne suka koma PDP yayin da wasu 4 daga jihar Osun suka koma sabuwar jam’iyyar
ADC ta Obasanjo. Ga jerin sunayen ‘yan majalisar da suka koma PDP din kamar
yadda jaridar Daily Trust ta rawaito;
Emmanuel Orker-Jev
Sani Rano
Barry Mpigi
Ali madaki
Dickson Tackighir
Hassan Saleh .
Danburam Nuhu
Mark Gbilah
Razak Atunwa
Ahmed Garba Bichi
Abdulsamad Dasuk
Zakari Mohammed
Canjin shekar ‘yan majalisar ta wakilai na zuwa
ne bayan mambobi15 a majalisar dattijai sun canja sheka PDP din, duk a yau.
Komawar ‘yan majalisar ya haifar da hargowa da hayaniya a zauren majalisar ta
wakilai, dalilin day a saka ‘yan jam’iyyar APC ficewa daga zauren majalisar.
DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku