JAMI’AN TSARO SUN TARWATSA MAGOYA BAYAN PDP DAGA WAJEN GANGAMI
Jami’an tsaro sun tarwatsa magoya bayan
jam’iyyar PDP daga filin gangamin da jam’iyyar zata yi gabannin zaben gwamna a
jihar Ekiti.
Mambobin jam’iyyar sun taru a shahararren wajen shakatawar nan na Fayuyi dake Ado Ekiti, babban birnin jihar a ranar Laraba kafin a fara harbe-harben bindiga a sama.
Bayan nan, Gwamna Ayodele Fayose yayi yunkurin jagorantar magoya bayan zuwa filin taron sai dai hakan bai yiwu ba bayan jami’an tsaron sun sake harba bindiga a sama.
Hakan ya sa an juya akalar taron zuwa harabar gidan gwamnati inda aka sanya ran Gwamna Ayodele Fayose da sauran shugabannin PDP zasu yi jawabi ga mambobin jam’iyyar.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku