BUHARI YA TAUSAYAWA WADANDA TASHIN GAS YA CIKA DA SU A KADUNA
Sakon shugaban kasar na kunshe ne a wata sanarwa daga babban
hadiminsa, Mallam Garba Shehu, a Abuja a ranar Lahadi.
Shugaban kasar yace yana jin radadinsu a wannan mawuyacin
lokaci, da kuma lura da asarar tattalin arziki wanda yan Najeriya masu kwazo
suka gina don ganin sun rayu cikin kwadago na gaskiya. Ya kara da cewa: “A
matsayina na mutum, ina sane da asarar da wannan hatsari ya janyo a rayuwar
wadannan yan Najeriya masu kwazo.”
Shugaban kasar ya shawarci yan Najeriya da su mayar da
hankali sosai wajen kula da bin matakan da suka dace a haraban kasuwancinsu. A
cewarsa, mayar da hankali wajen kula da matakan zai taimaka matuka wajen kore
duk wata annoba da zata taso.
A baya mun ji cewa a yammacin ranar Asabar gas ya tashi inda
ya kona shaguna 14 da wani dakin hada magunguna inda wani mutum daya ya ji
rauni a hanyar Ibrahim Taiwo Road dake unguwar Abeokuta a Kaduna.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku