BUHARI YA JAJANTA WA ‘YAN KASUWAR TERMINUS A JOS, JIHAR FILATO



Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jajanta wa al’ummar jihar Filato kan mummunar gobarar da ta lakume shaguna sama da 200 a kasuwar Terminus da ke birnin Jos, in da ya ce, ya kadu da wannan ibtila'in.
Wata sanarwa da mai taimaka wa Buhari kan harkokin watsa labarai, Garba Shehu  ya fitar ta ce, shugaba Buhari ya ce, ya kadu matuka da wannan ibtila’in da ya haddasa asarar dukiya mai tarin yawa.
Buhari ya kuma nuna damuwa kan cewa, a karo na uku kenan cikin shekaru 10 da irin wannan gobara ke barna a wannan kasuwa.
Shugaban ya kuma bukaci hukumomin da ke da ruwa da tsaki da su dauki matakan da suka dace wajen hana yawaitar aukuwar gobarar.
A yayin zantawa da sashen hausa na RFI, shugaban 'yan kasuwar Alh. Mustapha Ibrahim Bako ya ce, yanzu haka suna kan gudanar da bincike don gano musabbabin tashin gobarar wadda ta fara tun da misalin karfe 1 na dare a ranar Jumma’a.

DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA 
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/  
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv  
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A  nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com

Comments