BUHARI DA SHUGABAN KASAR AFRIKA TA KUDU SUN SAKA LABULE A FADAR GWAMNATIN NAJERIYA
A jiya, Laraba, ne shugaban kasar Najeriya,
Muhammadu Buhari, da takwaransa na kasar Afrika ta kudu, Cyril Ramaphosa, suka
yi wata ganawar sirri a fadar gwamnatin Najeriya dake Abuja.
Shugaba Buhari ya tarbi
Ramaphosa bayan isowarsa fadar gwamnatin Najeriya, Villa, da misalign karfe
3:00 na rana. Shugabannin biyu sun tattauna batutuwan game da suka kasashen da
suke shugabanta, musamman batun tattalin arziki da tsaro. A ranar 8 ga watan
Yuli ne fadar shugaban kasa ta koka a kan yawaitar hare-hare da ake kaiwa ‘yan
Najeriya dake zaune a kasar Afrika ta Kudu bisa wasu dalilai marasa ma’ana.
Mai taimkawa shugaba Buhari a bangaren harkokin
kasashen ketare, Abike Dabiri-Erewa, ta bayyana rashin jin dadinta bisa
salwantar rayukan ‘yan Najeriya a kasar Afrika ta Kudu.
Kamfanin sadarwa na MTN, mallakar kasar Afrika
ta Kudu, na fuskantar tirjiya da zanga-zanga daga ma’aikatansu da kungiyar
kwadago ta Najeriya a kan rashin mutunta ma’aikata da kulawa da hakkokinsu.
Shugaba Ramaphosa dake ziyarar aiki a Najeriya, zai kasance bako na musamman a
taron habaka cinikayya tsakanin kasashen Afrika karo na 25 dake gudana a Abuja.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku