ZANGA-ZANGA NA IYA KAWO TSAIKO GA AYYUKA A MAJALISAR DOKOKI



Domin nuna adawa ga sharuda 12 da majalisar dokoki ta bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari ya cika, wata kungiyar al’umma na yunkurin gudanar da zanga-zanga a harabar majalisa a Abuja, wanda ka iya durkusar da ayyukan yan majalisa a ranar Talata
A makon da ya gabata ne majalisar dokokin kasar, ta gindayawa shugaban kasa Buhari wasu sharuda 12 da take son yayi aiki a akai, bayan wata ganawa tsakanin majalisar dattawa da na wakilai inda yan majalisan suka yi barazanar tsig shugaban kasar idan yake aiki akan sharudan. Majiyoyi daga majalisar dokokin a jiya sun ce suna sane da shirin zanga-zanga da wata kungiya jama’a ke yi a ranar Talata, sannan kuma sun yi gargadin cewa idan aka bari hakan ta kasance babu abun da zai haifar sai ma gurguntar da ayyukan majalisar.
Anyi zargin cewa an dauki nauyin kungiyoyin ne domin su yi zanga-zanga akan majalisar dokoki tare da shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki a matsayin mutun na farko da za’a kaiwa hamayya
Kungiyar Dynamic Patriotic Citizens Group, ta hannun babban sakatarenta na kasa, Shehu Mohammed tayi zargin cewa an tanadarwa kungiyoyin dake shirin yin zanga-zangar tsaro damusamman daga sama. A halin da ake ciki, Sabuwar PDP kungiyar adawar APC ta bayyana cewa tana jiran jam’iyya mai mulki da shugaban kasa Muhammadu Buhari suyi kira gare su, sannan kuma ta tunasar da jam’iyyar cewa lokaci na shirin kure masu.


Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com

Comments