‘YAR MARIGAYI MKO ABIOLA TA BAYYANA CEWAR TSOHON SHUGABAN KASAR NAJERIYA OBASANJO BAI CI ZABEN SHEKARAR 1999 BA A NAJERIYA
Tudun Abiola, diyar marigayi MKO Abiola ta bayyana cewar
tsohon shugaban kasar Najeriya Obasanjo bai ci zaben shekarar 1999 ba a
Najeriya tare da bayyana cewar an dora shi ne a kan mulki kawai domin a kwantar
da hankalin Yarabawa a kan abinda aka yiwa mahaifin ta.
Tudun ta kara da cewar, sojoji ne suka dasa Obasanjo a kan
mulki domin ragewa ‘yan kabilar Yoruba radadin soke zaben Abiola na shekarar
1993. “An dora Obasanjo ne kawai a kan mulki, ba zaben sa aka yi ba. Ba a yi
zabe a shekarar 1999 ba, kawai an yi rantsuwa ne,” Tudun ta shaidawa gidan
Talabijin na Channels.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku