WATA KARUWA TA YAYYAGA WA WANI ‘DAN SANDA KAYA SANNAN TA GALLA MASA CIZO
Wadda ake tuhumar, wadda jami'an yan sandan
suka bayyana a matsayin karuwa sun ce ta takale su da fada ne saboda sun yi
kokarin kama ta. ‘Yan sandan sun bayyanawa kotun cewa, yarinyar ta yaga kakin
guda daga cikinsu inda kuma ta ciji dayan a lebbansa a lokacin da yayi yunkurin
sanya ta a cikin motarsu ta farautar masu laifi. Sun ce sai da suka hadu har su
uku a sannan ne suka samu damar kama ta har suka kaita ofishinsu, wanda daga
nan ne aka gurfanar da ita a kotun majistiri ta Isolo wanda kotun kuma ta bada
umarnin a tsare ta a gidan kaso.
Wannan al'amari ya faru ne a Otel din Okota
dake jihar Legas, wanda a nan ne wannan matashiya ke yin sana'arta ta
karuwanci. ‘Dan sanda mai gabatar da kara ya bayyana Kotun cewa, matashiyar ta
samu saɓani ne da wata abokiyar sana'arta wanda har ta kai ga ta dauko reza
tana mata barazana da ita. An yi kokarin ganin an kawo karshen rikicin amma
abin ya ci tura wanda daga nan ne aka bugawa jami'an yan sanda waya, suka zo
suka kama ta.
Alkalin kotun ta bada belin ta akan kudi Naira
dubu 100,000 bisa sharadin kawo wanda zai tsaya mata, amma kafin lokacin,
alkalin ta tisa keyarta zuwa gidan kaso har sai ta cika wadannan sharuda sannan
za a sake ta. Kana daga bisani ta ɗage karar zuwa 26 ga watan Yuli na shekara
ta 2018
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada
zumunta
Zaku iya turo mana
ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku