WASAN NAJERIYA DA ARGENTINA: WASA MAI TSANANI
'Yan
wasan kwallon kafa na Najeriya sun shawarci Super Eagles da su buga wasan da ta
dace da Argentina a yau Talata.
Peter Bewarang, Mai kula
da masana’anta na Hukumar kwallon kafa ta kasa ta NFF, Taiwo Ogunjobi, tsohon
sakatare janar na NFF, yace Super Eagles bata da wata hujja ko dalili da zai
hana ta cin Argentina.
A cikin ganawar da
kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a ranar Litinin a St. Petersburg a
Rasha, Bewarang ya amince da cewa Eagles na iya cin Argentina kai tsaye ba tare
da shakku ba, domin irin nasarar da suka samu na cin Iceland, ci biyu masu ban
haushi.
Najeriya zata kara ne da
Argentina a yau Talata a St. Petersburg a wasan karshe na rukuni na D a gasar
cin kofin duniya ta FIFA a 2018 a Rasha.
"Ya kamata su sani
cewa idan har suka kasa cin Argentina a wannan wasan, To, nan take zasu koma
gida, don haka su yi kokarin kada Argentina domin samun zarafin buga wasan
rukuni nag aba "in ji shi.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa Nijeriya
na da maki uku, idan suka fitar da Argentina ko suka yi kunnen doki a gasar,
zai basu damar shiga zagaye na biyu na wasan cin kofin duniya.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku