HARE-HAREN FILATO: OSINBAJO YA CE ZA A HUKUNTA MASU AIKATA LAIFI
Mataimakin
Shugaban kasa Yemi Osibanjo, a ranar Litinin, ya ziyarci Plateau bayan
hare-haren da ya haddasa salwantar rayukan jama’a.
A cikin kwanaki biyu da
suka wuce, an kashe mutane fiye da 80 a jihar daga hare-haren da aka kai a wasu
al'ummomi tara.
Osibanjo, wanda yake a
jihar don gane wa kansa halin da ake ciki da kuma hulɗa tare da shugabannin a
jihar, ya ce idan aka kama wadanda suka haddasa wannan rikic, zasu fuskanci
fushin gwamnati.
Ya ce an tura sojoji ne
domin kawo zaman lafiya a jihar.
"Shugaban Hukumar ‘yan
sanda ta kasa, IGP Ibrahim Idris ya tura ma'aikata zuwa Plateau kuma Babban
Jami'in Tsaro ya sanar da cewa za a tura Sojoji na musamman zuwa Filato.
"Sojoji na Musamman
za su taimaka wajen kokarin kawo zaman lafiya a jihar," in ji shi.
Rundunar Sojoji suna gudanar
da aikin tsaro na Operation Save Haven. Janar Abayomi Gabriel Olonisakin, ya ba
da dama da kuma izinin ƙarin Sojoji na musamman zuwa Jihar Filato don kawo
karshen wannan hare-haren.
Mataimakin Shugaban ya
bayyana bakin cikin sa kwarai da gaske game da cin galabar da ake yi wa jama’a
da basu jib a bas u gani ba.
A cewarsa, shugabanni ya
kamata su guje wa abubuwa da zasu haifar da maganganu ko ayuka da zasu haifar
da tashe-tashen hankula.
Gov Simon Lalong, a cikin
nashi bayanin, ya yi ta haɗaka tare da iyalan wadanda suka rasa 'yan uwa da
dukiya.
Lalong ya nuna bakin
ciki sosai saboda faruwan wannan lamari, Beroms da Fulani sun sanya hannu kan
yarjejeniyar kuma sunyi shawarwari game da yadda za'a zauna tare cikin lumana.
Ya gode wa Gwamnatin
Tarayya don ba da agajin gaggawa kuma ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za
ta taimaka wa jihar ta dawo da zaman lafiya a jihar.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku