BUHARI YANA SHIRIN KAMA NI - INJI OBASANJO
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo yayi
zargin cewa gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na kulla wani makirci
domin tsare shi har sai illa mashaa Allah akan tuhume-tuhume mara tushe.
Jaridar Premium Times ta rahoto cewa Obasanjo
ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya saki ta hannun kakakinsa, Kehinde
Akinyemi a ranar Juma’a, 8 ga watan Yuni. Yayi ikirarin cewa gwamnatin shugaba
Buhari shirin yin amfani da takardun karya da shedu na karya a kansa. Wannan
ikirari na zuwa ne yan makonni bayan musayar yawu da akayi tsakanin shugabannin
biyu, wadanda suka raba jiha bayan Obasanjo ya zargi shugaba Buhari da rashawa
sannan kuma ya shawarce shi da kada ya sake neman takara.
Buhari ya maida masa da martani ta hanyar
zarginsa da wawushe dala biliyan 16 na aikin wutar lantarki. Inda Obasanjo ya
maida martani a matsayin ikirarin rashin sani.
Da yake magana ta hannun hadiminsa a ranar
Juma’a, tsohon shugaban kasar yace shirin sa shi yin shiru ne yasa aka shirya makirci
wanda hukumar EFCC ta sake bude shafin bincike a ayyukan gwamnatinsa.
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku