Allah ya yiwa Ayuba Dahiru da aka fi kira
Tandu, jarumi a masana’antar shirya finan-finan Hausa dake Kano, rasuwa.
Da sanyi safiyar yau, Lahadi, ne marigayin ya
rasu a garin Kano bayan fama da gajeriyar rashin lafiya kamar yadda dareka a
masana’antar Kannywood, Falalu Dorayi, ya shaidawa BBC Hausa.
“Allah
ya yiwa Ayuba Tandu rasuwa bayan ya sha fama da zazzabi na kwana biyu. Muna
masu addu’ar Allah ya gafarta masa,” in ji Falalu Dorayi.
Kafin rasuwar sa, Tandu ya fi fitowa a
fina-finai ko matakin barkwanci. Wasu daga cikin fina-finan day a fito sun hada
da Auren Manga da Gobarar Titi da kuma Afrah. Ya rasu ya bar mata uku da kuma
yara 9.
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku