TSIGE SARAKI BA ZAI RAGE FARASHIN SHINKAFA ZUWA N7,000 BA – INJI FAYOSE


Gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, a ranar Laraba yace yana mamakin ko tsige Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattawa zai rage farashin buhun shinkafa zuwa N7,000 a kasuwan in Najeriya.




Fayose na martani ne akan kiraye-kiraye da ake yi kan tsige Saraki tun bayan da ya sauya sheka daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa PDP. Ya wallafa hakan ne a shafinsa na twitter wato @ayofayose. 

  • It is appalling that after more than three years of blaming former President Goodluck Jonathan and the PDP for their failure, they have now shifted their blame to Senator Saraki.


  • When a ruling party turns the removal of Senate President to its main agenda, the result is a heated polity. They are holding meetings upon meetings on Saraki’s impeachment as if removing the Senate President will reduce the price of rice to N7, 000 per bag that it was in 2015.


  • A halin da ake ciki, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adams Oshiomhole ya tirje akan cewa lallai sai shugaban majalisar dattawa, ya sauka daga matsayinsa ko kuma su tsige shi.


    Oshiomhole yace ba zai yiwu Saraki ya yi jagoranci ba alhalin APC ce ke da mafi rinjayen sanatoci a majalisar.



    DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA 
    FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/  
    TWITTER: https://twitter.com/northernstartv  
    https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/

    ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A  nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com
    DOMIN TALLA: http://northernstartv.blogspot.com/p/siyasa.html

    Comments