YA ZAMA DOLE ‘YAN NAJERIYA SU KAWO KARSHEN GWAMNATIN BUHARI A 2019 – ATIKU



Kungiyar yakin neman zabe na tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ta yi gargadi ga ‘yan Nijeriya da su tabbata ba su bari Buhari ya dawo mulkin Nijeriya a shekaarar 2019 ba.
Kungiyar ta Atiku Abubakar Campaign Organization ta bayyana alhininta bisa kisan gillar da ya afku a jihar Filato a baya-bayan nan, inda kungiyar ta bayyana lamarin da rashin kulawar gwamnati akan al’amuran da suka shafi al’ummar da ta ke mulki.

AACO ta ci gaba da cewa, gwamnati ta gaza wajen samar da canjin da ta yi ta wakar samarwa mutane a lokacin yakin neman zabe a sheakarar 2015.
Hasali ma dai sai talauci da ya karu, kashe-kashe ya yawaita, tattalin arzikinmu ya raunana da dai wasu abubuwa da dama da ke nuna gawawar gwamnatin nan, wadanda su ke nuna cewa Buhari bai dace da ci gaba mulkar Nijeriya ba a 2019.
Kodinatan kungiyar ta kasa, Dakta Fresh Onuoha ya shaidawa manaema labarai a jiya Litinin cewa, “Atiku Abubakar ne amsar matsalolin Nijeriya a shekarar 2019, domin gwamnatin Buhari ta gaza a kowane bangare na tafikar da harkar gwamnati.”
“Rayukan mutane a wannan gwamnati sam basu da wani muhimmanci sakamakon kisan mutane da ake yi babu dare babu rana da sunan wai fulani makiyaya, inda ita kuma gwamnati ta zauna turus, ta kasa tabuka komai.”
“Sam ba a sauraren jam’iyyun adawa da duk wani wanda zai fadi wata magana da ta saba da abinda gwamnatin ke ganin shi ne daidai duk kuwa da irin koke-koken da kungiyoyin jama’a ke yi babu dare babu rana. A yanzu ‘yan Nijeriya babu abinda suke yi sai kashe kawunansu saboda talauci.”
“Yunwa da talauci ya mamaye kasar baya ga cewa babu wani bangare na gwamnati da al’amura ke tafiya daidai. Lallai in har bamu tashi mun kai wannan gwamnati kasa ba, to kuwa za mu dawwama cikin yunwa da talauci.”
Ina kira ga ‘yan Nijeriya da su yi Buhari da tawagarsa korar kare su zabi Atiku a shekarar 2019 don samun rayuwa mai inganci.” inji Dakta Onuoha.

DOMIN KARIN LABARAI DA KARIN BAYANI KO TAMBAYA, A ZIYARCI SHAFUKAN SADA ZUMUNTA 
FACEBOOK: https://www.facebook.com/northernstartv/  
TWITTER: https://twitter.com/northernstartv  
https://www.linkedin.com/in/northern-star-television-6660bb162/
ZAKU IYA TURO RA'AYOYINKU 'A  nstv@tstvafrica.com KO northernstartv@gmail.com

Comments