Daya
daga cikinsu ta ce “wani malaminmu ya taba cewa yana so na, amma ko da na nuna
masa cewa ni ba wannan ne ya kawo ni makaranta ba sai ya yi min barazanar cewa
idan dai ban ba shi hadin kai ba, to ni ma lokaci zai zo da zan fado hannunsa.
“Ganin
cewa mun yi haka a dole na fasa daukar madda (course) dinsa saboda tsoron kada
na fada tarkonsa, kuma Allah ya taimake ni maddar tasa ba ta dole ba ce, don
haka kawai sai na ki dauka,” a cewar dalibar wadda ta nemi a sakaya sunanta.
A
nata bangaren, Jami’ar Bayero ta ce tana da ka’idoji masu tsauri na tunkarar
irin wadannan korafe-korafe.
Shugaban
sashin kula da jin dadin dalibai na jami’ar Dr Shamsudden Umar, ya shaida wa
BBC cewa makarantar na daya daga cikin wuraren da ba a daurewa irin wannan
dabi’a gindi, sannan ya nemi dalibai da kada su ji tsoro wurin bayyana duk
wanda ya nemi cin zarafinsu.
Haka
shi ma wani dalibi namiji, ya shaida wa BBC yadda ya fada tarkon wani malami
kawai saboda yana da alaka da wata daliba da malamin yake nema.
“Lamarin
sai da ya kai malamin da abokinsa suka kira ni har ofis suka titsiye ni kan alaka
ta da ita saboda suna zargin ta gaya mana cewa yana nemanta bayan da wata
kawarta ta kai mai tsegumi.”
Sai
da na je kare kaina, amma hakan bai yi wani tasiri ba,” a cewar dalibin wanda
shi ma ya nemi a boye sunansa.
Cin
zarafi ta hanyar lalata laifi ne a Najeriya, amma duk da haka ana ci gaba da
samun aukuwar lamura irin wannan a jami’o’in Najeriya.
A
kwanan nan ne wata dalibar Jami’ar Obafemi Awolowo ta tona asirin wani malamin
Jami’ar da ya nemi yin lalata da ita.
Dalibar
mai suna Monica Osagie ta nadi tattaunawar da ta yi da wani malaminta da ya
nemi yin lalata da ita domin ya ba ta damar cin jarabawa tare da watsa
tattaunawar.
Lamatrin
ya ja hankalin jama’a a ciki da wajen Najeriya.
Dalibar
ta Jami’ar Obafemi Awolowo, ta watsa tattaunawar tata ne da Farfesa Richard
Akindele, wanda ke koyarwa a sashin harkokin kasuwanci da hada-hadar kudi na
jami’ar, a shafukan sada zumunta.
Lamarin
dai ya kai ga jami’ar kafa kwamitin bincike wanda a karshe ya sami malamin da
laifi kuma aka kore shi daga aiki.
Mataimakin
shugaban jami’ar Farfesa Eyitope Ogunbodede, ya ce an kori Farfesa Richard
Akindele ne bayan da ya amsa laifin kulla alaka da daya daga cikin dalibansa ta
hanyar da ba ta dace ba.
“Farfesa
Akindele ya nemi yin lalata da Monica Osagie domin sauya maki kashi 33 da ta ci
zuwa adadin da zai ba ta damar tsallakewa,” a cewar Ogunbodede.
Kusan
wannan ne karo na farko da za a iya cewa wata makaranta ta dauki hukunci a
bainar jama’a kan irin wannan aika-aika da aka dade ana zargin wasu malaman
jami’a da aikata wa.
Kuma
babu shakka matakin da Monica ta dauka na tona asirin malamin ya samu karbuwa a
wurin daliban jami’a a sassan kasar da ma sauran jama’ar gari, saboda halayya
ce da ta dade tana faruwa ba wai a Najeriya kawai ba.
Sai
dai a cewar Dr Shamsudden Umar ya ce BUK ta bude wani ofis na musamman mai cin
gashin kansa domin bai wa dalibai damar kai korafe-korafe masu kama da irin
wadannan.
Ya
kara da cewa babu wani malami da za a dagawa kafa idan aka same shi da laifi,
yana mai bai wa dalibai kwarin gwiwa domin su bayyana duk wani bara-gurbin
malami da suka sani.
BBCHAUSA.COM
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku