BUHARI: KADA KU ZARGE NI GAME DA KISAN GILLAR FILATO
Shugaba Muhammadu Buhari ya nuna rashin amincewasa don zargin sa da ake yi
na na kashe 'yan Najeriya da ake makiyaya a sassa daban-daban na kasar da
aikatawa.
Buhari ya yi alwashin kare rayuka da
dukiyoyin al’umma da kuma hukunta duk wadanda aka kama da aikata wannan
mummunar aika aika.
Bisa ga nasa bayani kuma, Gwamnan jihar
Filato ya bayyana cewa sama da rayuka 200 aka hallaka a cikin hare-haren da aka
kai a yankunar.
Lalong ya ce hotunan kisan kiyashi da
na kare dangi da ake yi wa 'yan jihar marasa laifi, mata da yara suna ci gaba
da "azabtar da zukatanmu."
Shugaban ya yi magana a jiya a wani
taro tare da masu ruwa da tsaki a garin Jos, babban birnin jihar Filato, bayan
kisan da aka yi a wasu al'ummomi a jihar.
Wadanda ake zargi da zaton makiyaya sun
shirya kimanin awa 48 a kauyuka takwas na Gashish da Ropp a Barkin Ladi da karamar hukumar Riyom a jihar Filato suna kasha-kashe.
Ƙauyuka sune Xland,
Gindin Akwati, Ruku, Nghar, Kura Falls da Kakuruk duk a yankin Gashish da
Rakok, Kok da Razat kauyuka a gidan Ropp.
Yayinda yake mika ta’aziya ga
dangin wadanda suka rasa 'yan uwan su, Buhari ya ce kashe-kashen da aka yi a
Jihar Zamfara ya fi yawan na Filato, da Benuwe da ma wassu jihohi, inda ya
jaddada cewa kada jama’a su dauki kisan da ake yi a Filato a matsayin rikicin
addini.
Buhari ya bar Calabar, babban
birnin Jihar Cross River, zuwa Jos domin gane wa kansa halin da ake ciki bayan
kashe-kashen ranar Asabar.
Ya ce wadanda suka zarge shi da
cewa yaki ya yi Magana da masu kisan gillar wadanda ake zargin Fulani makiyaya
ba su yi masa adalci ba.
"Alal misali, halin da ake ciki a
Benue. Dik
wani manomi a Benuwe ya san cewa makiyaya a yankin suna amfani ne da sanduna
domin kiwo, idan kuma ya zama dole sai su dauki magirbi domin samar wa dabbobin
su abinci.
"Amma a yanzu an gaya mini cewa, wadan
da suka kai hare-haren suna dauke da AK47, kuma wadansu jama’a suna zargi na da
cewa ina goyon bayan masu wannan laifi shi yasa naki in yi masu Magana.
Wannan Magana babu adalci a ciki,
Ya ce: "Zan ci gaba da matsa wa
mambobin jami’an tsaro da ke ƙarƙashina domin daukar matakin tsaron rayukan
jama’a da dukiyoyinsu.
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku