AN KARA YAWAN 'YAN SANDA A JIHAR PLATEAU DOMIN KAWO KARSHEN TARZOMA
Hukumar
‘yan sanda ta kara tura yan sanda masu kwantar da tarzoma zuwa jihar Plateau
inda ake rikicin kare dangi, wanda mataimakin shugaban hukumar ‘yan sanda ta
kasa ya jagoranta domin kawo zaman lafiya a yankin Riyom, Barikin Ladi da kuma
Jos ta kudu.
Tuni
aka kai jirage masu saukan angulu guda biyu, Motoci masu dibar mayaka guda
biyar, Hukumar yan sanda CTU masu kwantar da tarzoma, da kuma yan sanda masu sa
fararen kaya.
Cikin
wadanda aka tura sun hada da hukumomin ‘yan sanda masu bincike da hukunta masu
laifufuka wato FCIID da kuma masu tarwatsa
da kuma lalata wadansu na’ura masu fashewa kamar su bam. EOD, Jami’an ‘yan
sanda masu amfani da karnuka domin gano masu laifi (K9) da kuma ‘yan sanda masu
yaki da ‘yan fashi SARS.
Rahotanni
sun nuna cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya yi alwashi cewa gwamnatinsa ba za ta
huta ba har sai an gano masu kisan da masu goyon bayan aikata laifin.
Mista Terna Tyopev,
kakakin rundunar 'yan sandan jihar Plateau ya ce an kashe mutane 86 ne yayin da
mutane shida suka jikkata.
Wadannan hare-haren sun
kasance a garuruwa 11 a gundumar Gashish a Barkin Ladi LGA da kuma wasu
al'ummomin da ke Bokkos da suka fara ranar Juma'a.
Don
haka, hukumar ‘yan sanda tana sanar da jama’a cewa idan sun sami labarin tashin
hankali, harbe-harbe, ko kasha – kasha a yankunan, sai su kira wadannan
lambobin wayar: 07059473022, 08038907662, 08075391844, and
09053872296’' domin daukar mataki nan take.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta
Zaku iya turo mana ra’ayoyin ku a nstv@tstvafrica.com
Comments
Post a Comment
Ku bada ra'ayoyin ku