MASARI YA SHAWARCI MUSULMAI SU YI ADDU'A DOMIN ZAMAN LAFIYA A WATAN RAMADAN


Gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari ya bukaci Musulmai su yi amfani da watan Ramadan don yin addu'a domin zaman lafiya, hadin kai da wadata a kasar da kuma duniya baki daya.
Gwamnan ya yi kiran a cikin wata sanarwa ta bakin Babban Mataimakin sa kan harkokin Labarai, Abdu Labaran, a ranar Alhamis a Katsina.
Musulmai a duniya sun fara azumin watan Ramadan a ranar Alhamis.
Ramadan shine wata na sha tara a kalandar Islama, kuma Musulmai a duk fadin duniya suna kama azumi don tunawa da farkon saukar Kur'ani zuwa Annabi Muhammadu.
Azumi shine ginshiƙan Musulunci na uku wanda Musulmai suke dakan kwanaki 29 zuwa 30 ta wajen hana kansu cin abinci, shan ruwa da kuma jima'i daga fitowar rana zuwa faɗuwar rana tare da bege na samun albarkun Allah.
Labaran ya bayyana abin da Gwamnan ya ce "Ina kira ga Musulmai na kasar nan su yi amfani da watan Ramadan don yin addu'a ga shugabancin kasar Najeriya.”
"Babu wata lokacin da za a keɓewa domin addu’a ga kasar Nijeriya fiye da yanzu, saboda matsalolin rashin tsaro da ke barazanar kasancewa.
"Dole ne mu sani cewa, shugabancin kasar nan ita ca jin dadin al'umma. wanda ke nufin ba za muyi fatan mugunta ga shugabanmu ba kuma muna fatan wadata ga al'ummar."
Masari ya yi kira ga 'yan Najeriya su ci gaba da tallafawa kokarin gwamnati na inganta yanayin rayuwar mutane da kuma matsawa kasar. (NAN)


Comments